HARAMTACCEN AURE PART 3
Sauri tayi ta tashi zaune, ciwon cikin ma taa daina ji.
"ki tashi kiyi break fast"
"Yaya majeeed me kakeyi har yanzu ba nasha maganin ba?"
"eeh anma ai bakici komai ba, donma kin samu an nuna miki kulawa?"
"naji anma dai ka fita zansha"
"indai kinason in fita sai kinsha koda tea ne, ko so kike a fara cewa ban kula dake?"
"wama zaisan banda lafiyan? Nidai nagode hakanan"
"Yanzu wani yasan ciwon ciki kike me zasuyi tunani?" yaja tsoki, itama shiru tayi bata k'ara cewa komi ba.
Bai hak'ura ba saida ya haɗa mata tea, sannan ya fita "Gobe in Umma ta k'ara tambayanki kice ban kaiki asibiti ba ko ban kula da cin abincinki" yanayin yanda yayi maganarne ya sakata murmushi, ko umma ce ta mishi magana?
Bai k'ara shigowa ɗakin ba, da rana yunwa ta isheta, gashi duk jikinta babu k'arfin da zata ɗaura girki, kuma tea yaa isheta hakanan, hakanan dai ta fito da nufin shiga kitchen ɗin ko zata samu abinda zataci.
A tsakiyar falon suka haɗu da plate a hannunshi shak'e da yankakkun fruit, ta ɗan kauda kanta zata wuce.
"ban ɗauka zakici abinci ba shiyasa na taho miki da fruit kawai" ta juya zata tafi
"shima na k'oshi fa" ta koma zata tafi, "tohh me kikeso a anso miki?" "ba komi fa" taci gaba da tafiyarta, rik'o hannunta yayi, tana niyyar k'wacewa suka jiyo sallamar Aunty zainab tana shigowa ɗakin da sauri ya saketa.
Kamar ta koma a ranta tace nifa shiyasa banson zuwa gidan yara, majeed yace, "sannu da zuwa Aunty" ta amsa tana niyyar zama
"Aunty kizo shigo daga ciki mana," ta matsa daga wurin Majeed suka wuce ɗakinta tare da Aunty zainabu" bayan sun zauna ne Aunty zainabu dai ta gaji da kallonta ganin dai k'arfin hali kawai take.
"Anma dai baki lafiya ko?"
"eeh anma naa warke"
"me akace yana damunki?"
"A'ah bamuje asibiti ba, ina dai jin...."
"kinajin me Majeeda? Zaki zauna da laulayi ne bazakuje asibiti ba kamar dai wacce batayi karatu ba?" maganar Aunty ma dariya ta bama majeeda,
"Aunty ciki kuma? Nikam kowah ma ya samin ido dole ne daga mace tayi aure sai haihuwa? Nidai ulcer tace ta ɗan tashi"
"ba dole bane anma don me ake auren? Karma ki fara sanyama ranki wannan, ni ba gashi ina jiran haihuwar ba Anma har yau Allah bai nufa ba"
"ni Aunty kima daina maganar nan"
"saboda me?" ta tsareta da kallon tuhuma, ta kasa magana, sai ga majeed yayi sallama ya shigo.
Suna gaisawa da majeed, Majeeda ta mik'e, "Aunty me za'a girka miki?" "kinga basai naci komi ba daman a hanya nake, garin damuna k'ara in sauri in wuce" cikin wasa majeeda tace "Aunty ko ruwa dai aka fara ai a gida kike, kuma dai yaune zuwanki na farko", "ina laifi ma da kika ganni?" majeed yace "ba laifi Aunty anma mudai yini mukeso" daria tayi sukaci gaba da fira harda majeed, sai da ya fita sannan ta jawo ledar magungunan mata masu kyau ta mik'a mata tana mata bayaninsu.
Saurarenta kawai take, ita dai ba buk'atarsu gareta ba, babu amfanin da zasu mata sai dai tayita ajiya kar tak'i amsa Aunty tayi tunanin wani Abun.
Aunty Zainabu bata daɗe ba ta tafi, Majeed ma lokacin ya bar gidan.
5:00...
Taji dai yunwar tak'i saurara mata, tun safe fa tea kawai tasha, daurewa tayi ta shiga kitchen ta fasa k'wai dai dai cikinta ta soya, sannan ta zauna falo ta cinyeshi tas tasha ruwa, sannan ta fara jin kanta.
Sai dai me, kamar abinda ciwon cikin ke jira kenan, tun kafin ta tashi daga wurin mararta ta fara wani azababben ciwo, dak'yar ta iya kai kanta ɗaki.
Ana gama sallahr isha'i ya shigo gidan, kai tsaye ɗakinta ya nufa har lokacin tana kwance da ciwon ciki.
Yaje inda take "Sannu ya jikin?" kai kawai ta ɗaga mishi "don Allah ka haɗamin ruwa mai zafi a toilet" da sauri ya mik'e ya tafi haɗa mata ko 5mnt ba'ai ba yace "gashi can" dak'yar ta mik'e tana tafiya, ya bita a baya yanaso ya rik'ota don gani yake kaman zata faɗi, sai da takai k'ofar har ta shiga taga bai koma ba cikin gatse tace "ko zaka taimaka min da wankan?" da sauri ya koma yabar wurin bayan ta rufe k'ofar.
Sai da ya tabbatar tasha magani, ya tsaya har barci ya ɗauketa sannan ya bar ɗakin nata.
Kwana biyun da tayi tana ciwon ciki duk shine yake kula da ita, wani lokacin sai dai ta tsaya tanata mishi kallon mamaki wai yaya majeed ne haka yake mata hidima,
Cikin kwana biyunnan ba k'aramin shak'uwa sukai ba, ko fita yayi yanzu yaa daina daɗewa zai dawo gidan koda bazasuyi magana ba, itama duk inda yaje a k'agare take ya dawo.
Ta gama kwanakin da take tayi wanka, yanzu taa samu sauk'i, anma duk da haka yana shiga ɗakinta yayi tsaye kawai bazaice komi ba, ko su haɗu falo kallo anma babu wani magana tsakaninsu.
Yau tun kusan da rana hadari ke haɗuwa yana washewa, shima ya hanata fita taje makaranta, anma har dare ba'ayi ruwa ba.
10pm.
Aka fara iska mai k'arfi, tana kwance ɗakinta bayan majeed ya lek'o ya fita, tayi shirin barcinta da er qaramar riga iya cibi mai hannu bra, sai sket ɗan qarami ko cinyoyinta bai gama rufewa ba, anma saita rufa cikin bargo fuskarta da hannuwanta ne kawai a waje, ta saka charge tana chatn.
Tunda aka fara iskan tayi kasak'e tama kasa chatn ɗin, abinka da jaharmu ta katsina😉 ana fara iskannan ba daɗewa aka ɗauke nepa, da sauri ta maida kanta cikin bargo tana jiran a tada Gen, wani irin tsoron da bata taɓa ji ba ya kamata, har aka fara ruwa a duk'unk'une take duk taa tsorata, ba shiri ta jawo zaninta dake gefe ta ɗaura sannan ta zura hijabinta, ta yaye bargonta a hannu da sauri ta nufi ɗakin Majeed tana haskawa da fitilan wayanta sai sauri take tana waige-waige, tana zuwa ta faɗa kawai sannan tayi sallama.
Yayi ɗai-ɗai saman gadonshi dagashi sai Vest da gajeren wando, ya ɗago yana kallonta duk tayi tsuru-tsuru da jingin kaya a hannunta, gajiya tayi da kalan kallon da yake mata tace, "an ɗauke wuta kuma naga ba'a tada Gen ba, nidai tsoro nakeji ni kaɗai gashi ana ruwa"
"Ɗakin naki ne kike tsoron kwana?" ta ɗaga mishi kai.
"tohh shknan ki kwanta anan bara in koma falo" ta ware manyan idanunta cikin ɗan hasken fitilan tana kallonshi.
"Inyi zamana a ɗakina mana, Ai wallahi falonma sai dai mu tafi tare" ta fara warware bargonta ta shimfiɗa gefen gadon da yake daga k'asa, ta buɗa wardrobe dinshi ta jawo wani bargon ta kwanta sannan ta rufa dashi duk yana kallonta.
Led lamp ɗinshi ya jawo zai kashe, "Don Allah yaya Majeed karka kashe hasken tsoro nakeji," ya maida ya ajiye sannan ya jawo bargonshi shima ya rufa duk sukayi shiru.
Can aka fara wata irin tsawa, ta wani k'ank'ame gadon cikin tsorata tana karanto addu'ar da akeyi in ana tsawa (subhanallazi yusabbihul ra'adi, bihamdihi walmala'kati min khifatihi) tana maida numfashi da sauri da sauri.
"kinga nifa bazaki hanamun barci ba da wannan tsoran naki, sai wani k'ara kike..." tun kafin ya rufe baki aka k'ara wata tsawar, batasan lokacin da tayi wurgi da bargon da take ciki ba ta haye saman gadon daman tuni taa cire hijabin jikinta, wurin hawan gadon zanin ya cire ta faɗa jikin Majeed ta ruk'unk'umeshi, yasa hannu zai cireta daga cikin shi ta k'ara rik'eshi tana jan numfashin tsoro, saitin kunnanshi take jan numfashin, gaba ɗaya taa gama rikita shi.
Tananan a jikinshi har aka gama ruwan saura yayyafi, anma duk da haka bata sakeshi, kallon k'irjinta yake yanda zuciyarta ke harbawa, komai nata a bayyane, ga wani irin k'amshi dake tashi ko ina a jikinta, ya fara kai hancinshi yana shinshinar wuyanta, ya saka hannunshi dai-dai cibinta yana shafa cikin, duk da ta shiga yanayi bai hanata rik'e hannun nashi ba, ko tsawa saurararta baiyi ba ya fara kissing ɗinta ta ko ina, yana sarrafa jikinta yanda yaga dama duk ya rikece.
Ita ɗinma ta fara manta a wacce duniyar take, tuni yaa rabata da duk wasu kaya dake jikinta, bata tashi tsorata ba saida taji yana niyyar shigarta, ta fara tureshi anma yak'i sakinta, harda ɗan kukanta "Yaya majeed ka daina, babu kyau fa", ya ɗago da jajayen idanunshi cikin sark'ak'k'iyar murya, "Plz majeeda kar muyi haka", cikin wata irin murya dake k'ara rikitashi "Nidai a'ah yaa maj...." ya hanata k'arasawa, ya haɗa bakinshi da nata, cikin kalan nashi salon mai rikitarwa.
Duk wani ihu da take tana tuttureshi harda cizo da yakushi bai tsaya saurara mata ba, baimasan tanayi ba har saida ya fara jinshi dai dai sannan hankalinshi ya dawo jikinshi, kwantawa yayi gefenta yana maida numfashi kamar wanda yasha gudu.
Kasa koda motsi tayi, har lokacin hawaye take, maido nepa da akayi ne ya sakashi mik'ewa ya haɗa mata ruwa mai zafi a toilet, yazo inda take ya saka hannu zai ɗauketa ta buge hannu, yaja baya, "kinga karki k'arama kanki wahala idan kin shiga ruwan zafi zaki rage jin ciwon" dak'yar ya lallaɓata ya kaita toilet ɗin, sai harararshi take, shikam dariya yake abinshi saboda wani irin farin ciki da yakeji.
Cikin kwamin wankan ya direta, taga yak'i ya fita, "me kuma kakemin anan" ya shafi gemunshi "wankan da kika tambayeni kozan taimaka in tayaki, shine zan miki",
"Haba Yaya majeed, plz nidai ya isa haka, ka ficemin plz", "tohm saikin fito, ga wani ruwan nan a bocket wanda zaki wankan tsarki" "naji" kawai tace da taga alaman in batayi magana ba bazai fice ba, sannan ta maida kanta tana jin wani yanayi daban.
40mnts later
Ta fito tana tafiya dak'yar, har ya gyara shimfiɗar ya canja zanin gado, ta kwanta gefen gadon sannan ta juya mishi baya, mirginowa yayi inda take ya kwantar da kanshi saman kafaɗarta ta tureshi muryarta da alaman kuka take tace, "wai me kakeyi haka Yaya Majeed? Kasanfa abinda kakeyi haramun ne" ya ɗan rage fara'arshi, bayan ya kamo hannuta yana wasa dashi "me nayi da ba dai-dai ba? Ɗazun da kika k'udundune a jikina na hanaki ne?" ya kai mata cizo a yatsanta daya saka a baki ta saki k'ara, da sauri takai mishi bugu a k'irji, "bafa wasa ake ba Yaya Majeed" sai kuma ta fashe da kuka sosai.
"Ka cuceni yaya majeed, shikenan ka rabani da abinda nake tak'ama da, yanzu wanne namiji ne zai aureni a haka bayan kai kamin saki uku? Zina fa kenan muka aikata, da wanda bai sona kuma"
"Bayan NI DAKE, wa yasan zina muka aikata? Kin manta duk duniya tana mana kallon miji da mata ne? NI DAKE ne kawai mukasan babu aure a tsakaninmu"
"Zamuci gaba da zama a haka ne? Kasan dai duk daɗewa dolene zanje na auri wani" hannunta dake rik'e a nashi ya ɗaura a bakinshi,
"ki daina faɗar haka plz, karki rabu dani Majeeda, sai yanzu na gane sosai ina buk'atarki a rayuwatah, wannan sirrine tsakanin NI DAKE, kinsan dai idan har iyayenmu suka san halin da muke ciki tsinuwa ne kawai, kuma dole su rabamu" ya marairaice fuska, "banson na rasaki a rayuwatah"
Tunda ya fara magana take kallonshi kamar wani zararre, anya Yaya majeed yana cikin hankalinshi? Baki a buɗe tace "HARAMTACCEN ZAMA zamuyi kenan?"
"kada ki zurfafa tunaninki mana, ki manta kawai da yanzu babu aure a tsakaninmu, ki kalleni a matsayin mijinki, tunda babu wanda yasan sirrinmu, muma mu manta abinda ya faru", hafsatul kiram ce ta faɗo mata a rai, ita kaɗaice tasan sirrinta da majeed, tohh anma yanzu ai basu k'asar sun tafi moscow ita da umar ɗinta, kuma ta yarda da ita bazata taɓa faɗama wani sirrinta ba.
"nidai bazan iya HARAMTACCEN ZAMAn nan ba, kowa yaci gaba da harkarshi kawai tunda daman ba sona kake ba, kawai sha'awanah kake"
"Waye ya faɗa miki bana sonki?" yayi saurin katseta.
"bai kamata wannan maganar ta fito daga bakinki ba, ni kaina bansan sanda na fara sonki ba Majeeda, anma ki yarda dani ina sonki, tun lokacin dana kasa ɗauke idanuna daga kallon kyakkyawar fuskarki a wancan ranar, na tsinci kaina da matsananci tausayinki a lokacin da kika fara rashin lafiya, har nakejin daman ciwon ya dawo a jikina, wannan ba so bane? Duk inda zanje koda na fita daga gida tunanina yana a kanki ta yanda bazan iya ɗaukar lokaci ba sai nazo na ganki, a hakan ba sonki nake ba?, da meyasa bana sha'awar jikinki sai yanzu? Idan har banisonki bazan taɓa sha'awarki ba, bansan yaushene ba ko kuma tayaya na fara sonki, anma na rantse da wanda raina yake a hannunsa ina sonki fiye da yanda nake son kaina,"
"kafin yanzu ina buk'atar, abinci, ruwa da iska ne kawai don in rayu, anma yanzu rayuwatah tana matuk'ar buk'atarki majeeda"
Share hawayenta tayi cikin farin ciki ta kwantar da kwanta a k'irjinshi, "nima ina sonka sosai yaya majeed" ya saka hannu yana shafa gashin kanta shima cikin jin daɗi yace, "Kin yarda zamuci gaba da zaman aurenmu?" ta ɗaga mishi kai.
Tasha barci sosai har 10 ta wuce sannan ta tashi, a hankali ta buɗe idonta tana kallon gefen da yake, bainan sai dai ta hango takardar daya mata rubutu a jiki "Good morning" ta ɗanyi murmushi sannan ta dire k'afafunta k'asa ta sauko ta fito falon tana tafiya a hankali, anan ma bainan ta wuce ɗakinta kawai.
Shiryawa tayi cikin wata haɗaɗɗiyar doguwar riga mai shegen kyau, da kaɗan ta wuce mata gwiwa, itama ɗan k'aramin hannu ne da ita, saboda yanda takejin jikinta bazata iya ɗaukar kaya mai nauyi ba, gashin kanta ma data tubke ji take duk ya mata nauyi, ta warwareshi kawai ta ɗan kwantoshi daga gaba, ga wani k'amshi da yake tashi ko ina a jikinta.
Da fara'arta ta fito cikin nishaɗi, har lokacin bai falo, ta wuce dinning table kawai hango kululon da ita a jere daman yunwa takeji.
Tana tsaye ta fara buɗa kulan farko farfesun kaza ne, na biyun kuma soyayyan dankali ne, tana cikin buɗewa taji an rungumotah ta baya, sannan ya sak'ala hannuwanshi cikin nata "kin tashi lafiya?"
"lafiya lau sannu da gajia" ya sakar mata kiss a wuya, ta nok'e tana daria sannan yace "gajiarme", "kasha girki mana"
"ba wani gajia tunda masoyiyatah na girka mawa" daria tayi sannan ta juyar da kanta ta kwantar a kafaɗarshi, "kema ya taki gajiyar?"
"gajiyar me?" ta tambayeshi yana daria sai so yake ta ɗago da fuskanta "kinaso in faɗa?" ta k'ara shigar da kanta a jikinshi tana daria "A'ah, nima ba wani gajia tunda masoyinah na faranta mawa" dariya suka yi dukansu, tace, "nifa Yaya Majeed na qagara naji girkinnan" a shagwaɓe tayi maganan, "yanzu kuwa," yaja mata kujera ta zauna, sannan ya zauna kusa da ita.
A plate ɗaya ya zuzzuba musu, ta ɗauko fork zata fara ci ya rik'e hannun, "daga yau wannan aiki nane" ta buɗa idanu tana daria, wata sabuwar soyayyar majeed na k'ara shigarta, ji tayi tafi kowacce mace farin ciki da samun Abokin zama wanda yake bata kulawarshi,
Haka yaci gaba da bata a baki har saida ta k'oshi, sannan ya langaɓe kai cikin wani salo "Saura ni", itama langaɓar dakai tayi "nifa bakacemun zanyi aiki ba" shikenan tunda bazaki bani ba, ni bama zanci ba ya tashi kamar zai tafi.
Dariya sosai ya bata tace "toh shikenan daman nasan ka k'oshi tun a kitchen" ya dawo da sauri ya zauna, "bazaki lallaɓani bama ko?" ta jawo fork ɗin, "anma sau ɗaya zan baka", ya marairaice "Yana iya tohh? Na yarda" ta ɗebo abincin ta nufi bakinshi dashi, saida ta kusan saka mishi ya buɗe bakinshi, sannan ta juyar da cokalin ta cinye tana daria "laah! Aikam bazan yarda zaki biyani ne" ya jawota yana k'ok'arin saka bakinshi a nata sai k'yalk'yatar daria suke.
Haka ya gama cin Abincin a shiririce, sunayi suna nishaɗinsu irinnan na ma'auratan gaskennan,
Ranar da yake friday ne bai fita office ba, wurinta ma babu maganar zuwa ckul, soyayarsu suka dinga sha kamarsu cinye juna, sai tarairaya majeeda takesha a wurin majeed, ko motsi zatayi tare suke motsawa😉 yananan lik'e da ita, kunsan irin farkon soyayyarnan.
Komai batayi ba ranar, girkin rana ma shine ya musu sai dai ya zaunar da ita falo ya kunna mata kallo, ta narkar da fuska a shagwaɓe tace "nidai banson kallonnan, k'ara muje can kitchen a tare ko bazanyi komai ba ina kallonka"
Ya kamo hannunta yana shafawa a fuskarshi "banso ki shigo kimin dariyan ban iya ba, kiyi kallonki, indai ninema bazan iya minti 2 bana ganin fuskarki ba, zan na fitowa" ta k'ara marairaicewa "nidai..." ya ɗaura hannunta a leɓenshi, "plz kiyi kallonki" ta ɗaya mishi kafaɗa sannan ya juya ya tafi girki.
Bai minti biyu zai fito ya sumbaceta cikin soyayya, sannan ya koma a haka harya gama girkin.
Da dare ne dai saiya fita ya musu take away, wannan rana ku biyu sun zame musu na farin ciki sosai.
Da dare suna zaune suna kallo a falo ta fara rufe ido alaman barci, sannan ta tashi daga jikinshi tana mik'a, "nidai saida safe" ya ɗago yana kallonta "barci?" ta ɗaga kai, "tohh bara in kashe kallon in taho" rausayar dakai sannan ta juya ta tafi ɗakinta, sai da tayi shirin barci sannan ta kwanta sai gashi ya shigo shima da shirin barcinshi.
"Anan zaka kwana?"
"ehh mana, in rama miki kwananki" murmushi kawai tayi har yahau gadon ya kwanta.
"nida na kwana a k'asa?" a hankali tayi maganar, ya jita anma sai yace, "me kikace?" Majeeda tace "bance komi ba"
Ya jawota jikinshi sannan yace, "anan dai kika kwana" sukai daria su duka, sannan ta juya mishi baya duk da amanne take a jikinshi.
Sun daɗe a haka, su basui magana ba, kuma ba barci suke ba, ya saka hannu ya kashe fitilan.
Tsawon lokaci sannan yayi magana a hankali "Meya hanaki barci" tayi shiru kamar mai barcin gaske batace komi ba, ya fara mata tafiyar tsutsa a wuyanta ta nok'e tana daria, "kice wani abu mana" inji majeed
"me zance?"
"wani abu mai daɗi"
"plx ka barni nayi barci"
"plx nima ki faɗamun yanda zanyi barci mai daɗi"
Ta nisa tana jan numfashi sannan tace, "Ina sonka Yaya Majeed, tabbas aurenah dakai bai cikin zaɓina, sai dai banson sanda soyayayarka ta cikamun zuciyah ba, kai namijine da kowacce mace zatai Alfaharin samu, fatana ko da yaushe in kasance tare dakai har k'arshen numfashina, ina sonka yaya Majeed, soyayyar da bata da iyaka, bazan daina sonka ba har Abada"
Ya k'ara rungumota jikinshi cikin jin daɗi farin ciki fal a zuciyarshi.
"nima ina sonki sosae Majeeda, ki kasance a tare dani, zan maye miki duk wani damuwarki da farin ciki, bazaki taɓa dana sanin kasancewa dani ba, ina sonki da yawa majeeda, don Allah karki barni" ya jawo hannunta bayan ya zare zoben hannunshi, ya saka mata, ta damk'e lallausan hannunta cikin nashi "zan kasance tare dakai har gaba da Abada yaya Majeed"
"Na shirya miki wani albishir gobe, anma bazan faɗa miki"
"plz mana yaya majeed"
"idanna faɗa miki bazai miki wani daɗi ba, kin gani da idonki" tace "tohh shknan" anma badon taso, duk tunaninta ta kasa gane ko Albishir ɗin menene, gashi ba ranar birthday ɗinta bane, ta hak'ura dai a haka barci ya ɗaukesu
8:35am
Ta fara farkawa, kallon bayanshi take bayan ta buɗe ido, ta murgina inda yaketa dubashi bai tashi ba, ta kwantar da kanta kawai a bayanshi tana jin soyayyarshi na k'ara shigarta.
Gani tayi kawai ya buɗe idanu sannan ya murgina ta koma k'asa, ya tallabo fuskarta yana kallon kyakkyawar fuskarta, itama kallonshi take suna ma suna murmushi, ta ɗan ɗago da fuskarta takai mishi kiss a goshi, ya lumshe ido ya buɗe cikin nishaɗi,
"kawai bana gajiya da kallonki" ta juyar da idanunta cikin jin daɗin abinda ya faɗa, sannan cikin narkar da murya tayi magana,
"tohh ka faɗamin magana" kiss ɗinta ya mayar mata sannan yace, "inasonki da yawa Majeeda"
"Nima ina sonka sosai"
Tare suka shiga kitchen, a shiririce suka haɗa break fast suna shan soyayyarsu, shi baiso tayi aiki, itama tafi so ita tayi, sai dai sukayi a tare kowah dai baison ɗan uwanshi ya wahala.
Tare suka zauna suka ciyar da junansu, sannan suka koma barci sai kusan azahar suka farka.
3:00pm
Suka fito da shirunsu, tana sanye da wani haɗaɗɗen material skye blue, ɗinkin riga da sket yayi matuk'ar amsarta, tayi kyau sosae da farin mayafi, sark'ar wuyanta ma fara, ba wani makeup tayi ba, anma kyau kam tasha shi.
Shima sanye yake da wani haɗaɗɗen yadi shima skye blue, ɗinkin yasha aiki mai kyau, ba k'aramin haɗuwa yayi ba, tabbas ba qaramin dacewa sukayi da juna ba.
Saida suka tsaya suka sha hotuna masu kyau, sannan suka jera suka fito tana kwance a jikinshi,
"wai ina zamuje?"
"wurare da yawa, yaune farkon fitarmu, har sai kince kin gaji" ta k'ara kwantar da kanta jikinshi.
"baka fiddo motan ba Yaya majeed yanzu sai naje can?" duk'awa yayi ya ɗaukota, suna tafiya yana kallon fuskanta cike da soyayya.
"kanaji dani da yawa"
"Kin cancanci fiye da hakan" sai da ya buɗe ya sakata, sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver, ya fitar da mota suka tafi.
Wurin siyar da motoci yayi parking, suka fito a tare tana duba wurin "kamar wurin saida motoci"
"lallai kifin rijiyace ke, motah zaki tayani zaɓe"
"wow! Anma dai kowace irice ka ɗauka red colour, ina sonta sosai"
"Akwai su da yawa, kedai muje ki zaɓamin"
"zan jiraka a mota plx"
"kin gaji?" yana ɗaga mata gira.
Ta ɗaga kai tana dariya, ya buɗe mata ta shiga motan sannan ya wuce wurin, ya ɗan ɗauka lokaci sannan ya dawo, yaja motan suka tafi.
A yana driving ma suna rik'e da hannun juna.
"Yaya majeed wai me zakayi da mota, bayan wanda kake da?"
Ya ɗan juyo yana kallon fuskarta, suka sakarma juna murmushi.
"banso wani ya k'ara ɗaukomin kene daga makaranta, plz karki k'ara shiga motan kowa, ga motanki nan idanma bananan"
Ta k'ank'ame hannunshi cikin tsananin farin ciki.
"dagaske motahta ce yaya majeed?"
ya ɗaga mata kai yana murmushi.
Wani ihu ta saki, sannan ta faɗa jikinshi, dole yayi parking a hanya.
"Nagode sosai yaya..." ya ɗaura hannunshi a saman leɓenta.
"babu godia a tsakaninmu, kinmin Abinda bazan iya biyanki da komai ba Majeeda, ina sonki da yawa, babu abinda bazan iya miki ba" ta ɗago fuskarta suna kallon juna,
"nifa ban ɗauka wani babban abu na maka ba Yaya majeed, anma nima ka sakani farin cikin da bansan yanda zan bayyana maka shi ba, kullum soyayyarka k'aruwa take a cikin zuciyatah"
"Kinason jin ta yanda zan gane kinyi farin cikin sosae?" ta ɗaga mishi kai cikin zumuɗi.
Ya matsa dai-dai kunnanta ya mata raɗa, ta ɗago suna kallon juna ya kanne mata ido.
"Rannan da zafi fa"
"wannan bazakiji ba, indai ba baki shirya faranta min ba"
"A'ah fa na yarda, anma sai gobe" ya ɗaga kafaɗa, "na yarda".
"Kina jin yunwa?" ta ɗaga mishi kai.
Ya juyar da motan suka nufi restaurant.
Suna cin Abinci suna firarsu, sai dariya duke, kallonsu kawai zakayi ka gane masoya ne dake matuk'ar son juna,
Alama ya mata da idanu data juya taga wasu tsofaffi mata da miji A bayansu, suma soyayyarsu sukesha kamar ba tsofi ba ko a nigeria, da jikanyarsu y'ar yarinya mai kyau, A hankali yace mata,
"na k'agara mu zama kamar tsofinnan"
"nima sun burgeni sosae"
Sun gama suna fitowa suka haɗu da Aisha a hanya, tun kafin su ganta ta tsaya tana kallonsu, hannunsu mak'ale da juna, suna tafiyarsu gwanin sha'awah zuciyarta sai bugawa.
Majeeda taa rigashi ganinta, itama saida k'irjinta ya fara bugawa wani irin kishinta takeji, ta fara k'ok'arin zare hannunta daga nashi, ya rik'eta tsam don shima yaga Aishan, har sukazo suka wuce inda take tsaye kamar bai ganta ba, ta juya taci gaba da kallonsu har suka shiga mota.
Batace mishi komi ba, anma duk jikinta yayi sanyi, shikam baima nuna mata alaman komi ba yaci gaba da janta da fira har saida yaga hankalinta ya kwanta.
"plz Yaya Majeed muje gidansu momie da gidansu Umma"
"Marece yaa farayi sai dai gobe" ta marairaice fuska.
"kaifa kace saina gaji"
"nifa naso mu koma gida, anma ki zaɓa ɗaya dai"
"nidai tohh muje gidan Umma na daɗe banga zahra ba"
"Gidan momie zamuje nan kika daɗe bakije ba"
"Duk yanda kace mijin gidanah" ya harareta da wasa
"mijin gidanki ma ba mijinki ba?" tayi daria sosai,
"hakane mijina, kuma MASOYINA NA HAR ABADA (mrs Umar)"
"gsky naji sunannan yaimin daɗi"
Text ya shigo a wayarshi, tana hannunta tana game, shi kuma yana driving.
"Dubamun text ɗin waye?"
Tayi minimizing sannan ta shiga duba text ɗin, sai da kanta ya sara ganin mai turowan, anma tadai dake.
"karantamun mana" da ɗan washe fuskarta ta fara karanta mishi,
"Wai honiee yaushene zaka daina wahalar da zuciyatah ne? Yanzu don kana tare da wannan banzar matar da bama son ta kake ba zaka shareni" ta k'yalk'yale da daria bayan ta gama karantawa,
"ke kuma miye na daria, sai akace miki ki karanta duka, Aisha ce ko?"
"harma akwai wata bayanta kenan? Nifa aka mawa ba kaika ba, da gaske dariyar ta bani"
"nidai naji haushi, ba tun yau ba nasan kina sane da bata gabana"
"yanzunma ban tambaya bafa"
"tohh nayi shiru matar gidana" sukai dariya lokacin sunzo k'ofar gidansu, aka buɗe mishi gate suka shiga.
Tare suka jera suka shiga falon momie na sallama da bak'uwa, ganinsu da tayi tare tama kasa ɓoye farin cikinta, tayi saurin sallamar bak'uwar ta taho sai k'ara washe baki take,
"tare kuke tafe?" Majeed ya shafa gefen gemunshi ya silalo daga saman kujerar kanshi a k'asa yana gaisheta, Majeeda ta koma inda take ta kwantar da kanta jikinta,
"Momienah inata kewarki"
"ba gashi yanzu kinzo kin ganni ba?"
"ba irin haka ba momie, gidannan ma dukanshi ina kewarshi"
"Rabani da shagwaɓarnan taki, kunyi sa'a ma daddynku yana gida"
Ta tashi tana murna,
"Anma naji daɗi sosae momie bara naje in gaisheshi"
"Tohh ɗiyar daddynta" yanayin momie kawai zaka kalla ka gane tsantsar farin cikin da take ciki.
Majeeda da Majeed tare suka jera suka shiga falon Abba, shima yaji daɗin ganinsu sosae a tare, ya dinga sanya musu Albarka.
Sannan gabanta ya shiga faɗuwa, tama kasa haɗa ido da Abba, duk a tsorace take gani take kamar zai iya gano abinda suke ciki, duk jinta take wata daban,
Ta gaya musu kyautar motar da Majeed ya mata, suka dunga mishi godia sosae,
Majeed ya lura da sukukun da Majeeda tayi, duk hankalinshi na kanta, basu daɗe ba suka tafi.
